Thursday 25 June 2020

MARTABAR HIDIMAR MASU BIN ALMASIHU (3)




Mutanen da ba sa son su dogara ga Ubangiji suna tunanin za su iya yin komai a cikin ikon kansu da kuma iliminsu. Wannan ko dai tawaye ne, girman kai ko kuma jahilci!

Bari mu yi zurfin nazari a kan koyarwa da hidimar Almasihu Yesu wanda har yanzu yake da matukar nacewa a kan bangaskiya!

Bari mu dubi wadansu ayoyi don karfafa  abubuwan da muka ambata a sama.
Ubangijinmu Yesu yana wa masu sauraronsa kashedi a kan marasa bada gaskiya har da mu na zamanin yanzu;
 "To, ga shi, Ubangiji yana ƙawata tsire-tsiren jeji ma haka, waɗanda yau suke raye, gobe kuwa a jefa su a murhu, balle ku? Ya ku masu ƙarancin bangaskiya!" (Mat 6.30)

 Dole ne mu koyi dogara ga Ubangiji game da dukan  al'amuran rayuwa. Kamar dai yadda ya ke magance bukatun dukkan halittarsa wadanda basu yin gwagwarmaya, haka ya fi kulawa da dukkan masu bangaskiya gareshi.

A wani sharhi na bangaskiya, Kiristi Yesu ya ji dadin bangaskiyar wannan jarumin;
 "Da Yesu ya ji haka, sai ya yi mamaki, har ya ce wa mabiyansa, 'Gaskiya, ina gaya muku, ko a cikin Isra'ila ban taɓa samun bangaskiya mai ƙarfi irin wannan ba.'"
(Matta 8:10)
Bangaran ban sha'awar bangaskiyar jarumin yana cikin kalmominsa ga Yesu a cikin aya ta takwas; ".. .amma sai ka yi magana kawai, yarona kuwa zai warke." Ya gaskanta da ikon Maganar Kiristi da ya isa ya kai gun bawansa mara lafiya har ya warkar da shi.

Wannan shi ne irin bangaskiyar da ake bukata  daga kowane mai bin Yesu Almasihu!
Almajiran Yesu sun kasa fitar da aljannu daga wani yaron da aka kawo masu;
 "Sai Yesu ya amsa ya ce, 'Ya ku tsara marasa bangaskiya, kangararru! Har yaushe zan zama da ku, ina jure muku? Kawo ɗa naka nan.'"(Luka 9:41).

Daga baya, almajiran suka tambayi Yesu ko me yasa ba su iya fitar da aljanun ba.
"Sai ya ce musu, 'Ai, irin wannan ba ya fita sai da addu'a da azumi'” (Markus 9:29)

Yawancin masu bi sun kasa aiwatar da hidimar Kiristi saboda rashin bangaskiya. Addu'a da Azumi na iya motsa karfin bangaskiya da ikon Ruhu Mai Tsarki don hidimar mu'ujizai. Ubangiji ya ceci  kowane mutum, ya kuma kira shi ya kuma kebe shi domin aiki cikin bangaskiya ta ikon Ruhu a cikin sunan Yesu. Tamkar, wannan shine matsayin kowane Kirista.

Bari mu yi addu'ar farkaswar bangaskiya da na zubowar  Ruhu Mai Tsarki don martabar hidimar Kiristi ya sauko kan Ikilisiya don cikakken aiki a cikin jama'ar Ubangiji. Amin

MARTABAR HIDIMAR ALMASIHU CIKIN IKILISIYA (2)






Menene zai iya zama dalilin wannan mummunar aikin sabo da kuma ɓarna daga misharorin farko? Za mu tattauna wannan tambayar a cikin wata littafinmu na gaba.
Bari mu dawo kan batun tattaunawar da muke ciki. Bangaskiya ce kadai ingantacciyar hanyar sadaukar da kai na ruhaniya ya zamar wa mutanen Ubangiji wajibi. Ba za mu taba yin wasa da shi ba ko kadan. Saboda danganta da Ubangiji wanda shine Ruhu ba zai iya aiki ba sai ta baiwar Bangaskiya ta Ruhu Mai Tsarki. Babu abin da za mu iya sai ta hanyar bangaskiya da ayyukanta. Ba da Gaskiya kadai shine Amsa! Ya zama dole a dawo kanta!
Ubangiji Maɗaukaki ya fusata game da zunubin rashin bangaskiya, "Ya ce, ‘Zan ɓoye musu fuskata, Zan ga yadda ƙarshensu zai zama. Gama su muguwar tsara ce, 'Ya'ya ne marasa bangaskiya."
(M/Shari'a 32:20).
Dukkan albarkun Ubangiji na samuwa ta wurin bangaskiya. Kuma duk waɗanda suka ba da gaskiya ga Ubangiji daga tsara zuwa tsara sun sami mu'ujizai, da kuma abubuwan al'ajabi da yawa na wadata. Amma waɗanda suka zaɓa su yi taurin kai cikin rashin bangaskiya ma sun dandana wahaloli da matsanancin talauci!
 "Wanda zuciyarsa ba daidai take ba, zai fāɗi, Amma adali zai rayu bisa ga bangaskiyarsa."
(Hab 2:4)

MARTABAR HIDIMAR ALMASIHU CIKIN IKILISIYA



Na ɗade da damuwa game da batun Bangaskiya da Ruhu Mai Tsarki a cikin Ikklisiya tun lokacin da aka fara Bisharar Kiristi ta hannun mishanari na farko tsakanin kabilunmu da al'ummominmu daban-daban.

Idan aka kwatanta da koyarwar Kiristi a cikin Bisharu huɗu na Sabon Alkawari, Ikilisiyoyi da yawa sun sami koyarwar da ba ta dace ba wanda ya sa ake ganin Bishara ta hanyar da ake tuhumarta.

Ga takamaiman bayani, koyarwar Kiristi na warkarwa (Mt 10:1,8) ta gurbanta ta dalilin kimiyyar likitanci. Sabanin Ilimin Kristi da hikima ta wurin Ruhu Mai Tsarki (Luka 4:32) aka sauya da ilimin boko. Aka sauya ikon kawar da aljanu (Markus 6:13) da hanyar ilimin asibitocin mahaukata da kimmiyyar nazarin tunanin mutum. A kashin gaskiya, Bangaskiya watau baiwar Ruhu Mai Tsarki da rayuwar Kiristi an yi watsi dasu gaba ɗaya kuma an watsar da su!

Shi ya sa duk da Littafi Mai Tsarki a hannayen masu dubin yawa, Kalmar Ubangiji ba ta iya karɓuwa balle ta kasance mai amfani ga yawancin zukatan mutane.

Wannan mawuyacin halin ya bar Kiristoci da yawa cikin halin ruɗani har ya kai ga ko su gaskanta Kiristi ko kuma koyarwar wadanda suka kafa Ikilisiyoyin. Ubangiji Madaukaki mai jinƙai ne, ba zai taɓa barin zaɓaɓɓunsa a  cikin wannan rudani ba!

Monday 15 June 2020

MULKIN ALLAH A DUNIYA



Dauki mintoci kaɗan ka karanta addu'ar da Kiristi Yesu ya gabatarwa masu binsa; watau, Addu'ar Ubangiji.

“...Ya Ubanmu, wanda yake cikin Sama, A kiyaye sunanka da tsarki. Mulkinka yă zo, A aikata nufinka a duniya kamar yadda ake yi a Sama.” (Mt 6: 9, 10)

Menene fahimtarka, fassararka da amincewarka game da “... A aikata nufinka a duniya kamar yadda ake yi a Sama ...”? Amsarka zai tabbatar da yadda kake morar wannan Addu'ar a cikin rayuwarka ta yau da kullun

Mun nace kan wannan batun domin wahayi ne da ya dade kuma ya kasance a birnin zuciyar shirin Ubangiji ta wurin Kiristi don ya ba Ikilisiyarsa da al'ummar duniya matsayin karshe cike da nasara da ikon cikin hali na karshen da ake ciki. Wutar farkaswar na kan ci, babu mai iya tsayarda ita, kuma mutane da yawa sun kamu da harsunan wutar da za ta mayar da tsarin Mulkin Allah a gurbin ta a cikin duniya!

Fidda zuciya, rudani da rashin bege a bayyane suke a fuskokin mutane da yawa a duk fadin duniya a yau! Sai kuma tsananin Kaunar Duniya ta rinjayi mutane masu yawan gaske, dogara ga Ubangiji ya rasa fifiko a tsakanin mabiyan Almasihu. Wannan shine ya jawo la'ana da ba'a da kunya ga Ikilisiyarsa.

Kowane mai gaskiya a Ruhaniya zai iya gane da abin da ke gudana game da wannan halin koma baya da lalacewar; sai ga Magadan Ubangiji da ake tsammanin za su wakilce shi ta bayyana ikonsa, sai aka mai da su abin zargi a fuskar duniya!

Me ya sa haka? Gaskiyar ita ce, idan tsarin duniya ya fi mallakar mutanen Allah, kuma muddin an yi watsi da ƙa’idodinsa da tsayayya da Maganarsa da ke kunshe cikin hidimar Kiristi, to, bin Yesu sai ya zama kamar addinin na al'ada, ba hanyar Gaskiya na ceton rayuka ba kuma. Wannan ya haifar da abin da ke faruwa a fagen siyasar duniya a yau wanda ya mamaye al'amuran Ikilisiyar Almasihu!

MULKIN DUNIYA GABA DA MULKIN ALMASIHU

Wannan batun yana buƙatar cikakken bayani da bincike. Amma a halin yanzu, gwargwadon wahayi na Ruhaniya da tabbataccen kwarewarsa, Gaskiya ba ta da wuyar samu da kuma bayyani!

Ta yaya Ikklisiya ta shiga siyasar duniya? Domin hidimar Kiristi da ka'idodinsa na Mulki a bayyane dalla-dalla suke. Ta yaya za a sami makarantun Kirista, sai a tartar don koyar da ilimin duniya da wayewa zamani ciki? Me ya faru da horarwar da ginuwa ta Ruhaniya, gwargwadon ainihin hanyar da Ubangiji Maɗaukaki ya yi tsari ta wurin Almasihu Yesu?

Me yasa duniyar marasa imani zata ƙirƙiro tsarin siyasa sa'annan ta gayyaci Ikilisiyar Almasihu ta sa hannu da kuma aikata ko gudanar da ita? (Wani lokacin ina mamakin ko ma akwai Kirista a wannan yanayin da farko!). Idan da farko mishaneri da majami'u 'yan asalin sun nace a kan bayyanar Mulkin Almasihu wanda aka bayyana a sarari cikin koyarwarsa a cikin Matiyu sura 5,6, & 7, da sauran nassoshi na Littafi Mai Tsarki da suka nanata batun gudanar da Mulkin Sama a Duniya, shin za a sake samun buƙatar zaɓin madadin wani abu da ake kira siyasa kuma?

Addu'ar Ubangiji ta kasance tare da mu tun daga lokacin da Almasihu Yesu ya ba da shi ga almajirai waɗanda su kuma suka mika ta zuwa ga Ikilisiyarsa. Tun daga wannan lokacin sai Addu'ar ta kasance haddacewa ne kawai, ko waƙa ko kalmomin ƙarshen taron sujada kawai! Ko da yake wannan batun ya kasance da tsawon shekaru da yawa, amma, don Daukakar Ubangiji, lokaci yayi da za a dawo kan aikin gaskiya da kuma amfani da shi!

Babban hakkin Mulkin Sama a Duniya shine tasirin da Addu'ar Ubangiji ya mika wa Ikklisiya da ya kamata ta yi a rayuwar wadanda suka yi himmar nacewa a kai da kuma aikata shi.

Bari wannan Addu'ar Samaniya ta mamaye duniya. Domin muna shelar Addu'ar Ubangiji tare da bangaskiyar samun fa'idodin sa na gaskiya a rayuwarmu da mulkin sa a kan duniya, wannan shine abin da Almasihu yayi nufin bada shi garemu.

"Mulkinka yă zo, A aikata nufinka a duniya kamar yadda ake yi a Sama"
(Mt 6:10).
Sama a duniya; kamar yadda muka furta Kiristi a duniya haka kuma a sama za a furta mu. Yadda kuma aka yi musunsa a nan duniya haka kuma za a yi musun mutum a Sama. (Luka 12: 8, 9)

Sama a duniya; Akwai wannan tabbacin cewa sama za ta aikata duk abin da muka yanke shawarar yi muddin akwai yarda game da abin muka kulla a nan duniya. Bangaskiyar shaidu biyu ko uku na iya tabbatar da amsawar Ubangiji ga addu'a da aikinsa a zahiri. (Mt 18: 18-20.)

Sama a duniya; "Hakanan ina gaya maku, akwai farin ciki a gaban mala'ikun Allah kan wani mai zunubi da ya tuba." (Lk 15:10.)

Sama a duniya; Tabbacin shiga Kursiyi ko Mazaunin Ubangiji Madaukaki cikin Almasihu cikin murna da Madawwamin farin ciki...
(Ibraniyawa 12: 22-24).

Sama a duniya;
“...Su ne waɗanda suka fito daga matsananciyar wahala, sun wanke rigunansu, suka mai da su farare da jinin Ɗan Ragon nan....suke a gaban kursiyin Allah, suna bauta masa dare da rana a Haikalinsa. Na zaune a kan kursiyin nan kuwa, zai kare su da Zatinsa,"
(W. Yah 7.14-15)

Sama a duniya:
"...Sama kursiyina ce, duniya kuwa matashin sawuna ce. Daga nan wane irin gida za ku iya ginawa domina, wane irin wuri ne kuma zan zauna?"
(Ishaya 66: 1).

Tsarin Ikilisiya na duniya ba ya nufin komi ga Ubangiji; ginin gidan mu na ruhu ko zuciyar mu ya fi muhimmanci gareshi!

Sama a duniya; mu adana dukiyarmu a Sama; Zukatanmu kuma su kuɓuta daga jarabobin kayan duniya da munanan ayyukanta. (Mt 6: 20,21; 19:21.)

Sama a duniya; “...“Halleluya! Yin ceto, da ɗaukaka, da iko, sun tabbata ga Allahnmu,
(W. Yah 19.1)

Gama Mulki da Iko da Girma na Ubangiji ne, daga yanzu har matukar zamani! Amin kuma Amin!

Tuesday 9 June 2020

GOD'S KINGDOM ON EARTH



This is one of the tracts among many awaiting printing. Thanks and Blessings for praying along to God's Glory. Amen!

Take a minute to recite this powerful Heavenly prayer gift by Christ Jesus to His believers;

“...Our Father in Heaven, Hallowed be Your Name.
Your Kingdom come.
Your will be done on earth as it is in Heaven...” Mt 6:9, 10

What is your understanding, interpretation and conviction of “...Your will be done on earth as it is in Heaven...”? Your answer will determine your response and action about it in your daily life expression and experience.

We insist on this long existing power pack revelation because it had been and is still the present heartbeat of God’s plan and mission through Christ to give His church, the believing community of the world a final back-slap in its coma state. The fire brand revival is unstoppably ensuing and many are catching its tongues-faith-flames to be Restored to God's Kingdom arrangement here on Earth!

The desperation on the faces of many in all nations of the world is a clear evidence of hopelessness, despair and confusion. Worldliness had played a major part in ruling many; and disappointments and utter futility had mounted higher than expected!

Every Spiritual upright can easily discern what informed this state of derail; God's heirs expected to represent Him in authority and power had been made the object of ridicule in the face of the world!?

The Truth is, the world system controls God's people if His laid down standard and principles were ignored, rejected and despised. When God's Word in Christ's ministry is resisted, conventional religious ‘Christianity' takes to the centre stage. This had resulted to what is happening in the political scene in the world today!

WORLD POLITICS VS GOD'S KINGDOM
This topic needs an elaborate approach and research. Meanwhile, based on Spiritual inspiration and definite experiences, the Truth is not hard to find and expressed!

How did the church get involved in partisan politics? It is because Christ's ministry and His Kingdom principles were mistakenly or deliberately misinterpreted. By the way, how can you have a Christian school only to teach and practice secular knowledge in it? What happened to the Spiritual discipline, exercise and growth according to the exact approach by God Almighty through Christ Jesus?

Why should the unbelieving world invent a political order or system and invite the church for participation? (Sometimes I wonder whether there had been Christians in this aspect in the first place!). If the early missionaries and the indigenous churches had insisted on Christ's Kingdom orientation which are clearly defined in His teachings in Matthew chapters 5,6,&8, and other references of the Holy Bible, would there be the need for the wrong alternative called politics?

The Lord’s Prayer had been with us since the time Christ Jesus freely gave it to the disciples who in turn passed it on to the church. Since then it had been a mere recitation, chorus or doxology at the end of church gatherings! Though it had been for long decades, but, for God's sake, it is time to get back to the reality practice and application of it!

The most fundamental assignment of Heaven on Earth is the impact the Lord’s Prayer handed over to the church ought to make in many lives who profess or recite it.
Let this Heavenly prayer make impact in the world. Because we declare the Lord’s Prayer with the faith of earning its reality benefits in our lives and its rule over the world, that was what Christ meant by what He said;
“...Your will be done earth as it is in Heaven...” (Mt 6:10.)

Heaven on earth; as we confess Christ on earth so in heaven we shall be confessed; the same with His denial here on earth so shall men be denied in Heaven. (Luke 12:8, 9)

Heaven on earth; there is assurance of Heaven complying with and acting upon our decisions to bind and loose anything here on earth. The faith of two or three witnesses can compel divine response to prayer and His presence in reality. (Mt 18:18-20.)

Heaven on earth; "Likewise, I say to you, there is joy in the presence of the angels of God over one sinner who repents.” (Lk 15:10.)

Heaven on earth; the definite declaration of our arrival to the Heavenly composition and we being partakers of the inheritance of God... (Hebrews 12:22-24).

Heaven on earth; the saints adorned in glorious attire washed by the precious Blood of the Lamb of God assigned to worship Him day and night who is seated on His Throne in the midst of them. (Rev 7:13-15.)

Heaven on earth:
“...Heaven is My throne, And earth is My footstool.
Where is the house that you will build Me? And where is the place of My rest...” (Is 66:1).

Earthly church structures mean nothing to God; our Spiritual or heart temples concern Him most!
Heaven on earth; let us secure our treasures in Heaven; our hearts shall also be secured and protected from evil attack or spoil. (Mt 6:20,21; 19:21.)

Heaven on earth; “...Alleluia! Salvation and glory and honor and power belong to the Lord our God!” (Rev 19:1.)
For God's is the Power, Honour and Glory forever and ever. Amen!

Contact Address:
Brother Matthew Arin Adams
Boiling Point Gospel Centre, Uphill Opp Jevicho Filling Station, Bauchi Ring Road, Jos Nigeria. Email: revivingnigeria@gmail.com +234 803 703 5048
neworientation1.blogspot.com
www.boilingpointgospelcentre.ng